fidelitybank

Gwamnoni sun amince da wa’adin watanni su cigaba da karɓar kuɗin ƙananan hukumomi

Date:

Gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi, sun cimma matsaya a kan ba wa jihohi wa’adin wata uku kafin su tsame hannnunsu daga lamurran ƙananan hukumomi.

Hakan dai ya biyo bayan damuwar da jihohin suka nuna game da ba wa ƙananan hukumomin ‘yancinsu nan-take saboda tasirin da hakan zai yi kan albashi da kuma wasu abubuwa da suke tarraya a kai.

Wannan dai na nufin ya zama dole ƙananan hukumomin su jira har nan da watan Oktoba kafin su fara samun kuɗaɗensu kai tsaye.

Gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya, ya shaida wa BBC cewa, daga cikin abubuwan da aka tattauna yanzu an ba wa jihohin da basu yi zaben ƙananan hukumomi ba damar su yi zaɓe, sannan wannan doka ta fara aiki, domin idan aka ce a fara ba wa ƙananan hukumomi kuɗaɗensu to inda ba a yi zaɓe ba wa za a ba wa ke nan?

Baya ga ba wa jihohi damar gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi, za su kuma kawo tsare-tsarensu domin akwai abubuwa da akwai haɗaka a ciki a tsakanin jihohi da kuma ƙananan hukumomi kamar ɓangaren ilimi wato hukumar SUBEB, da ɓangaren lafiya a matakin farko to shi ya sa aka bada dama saboda kada a samu matsala.

Gwamna Yahaya, ya ce kuma suna fatan zuwa watan Oktoban jihohin da basu yi zaɓe ba sun yi, sai doka ta fara aiki.

Masu sharhi kan lamuran yau da kullum na ganin ba wa ƙananan hukumomi ƴancin cin gashin kai ne kawai zai iya kawo karshen matsalar Najeriya saboda su ne suka fi kusa da jama’a kuma su suka fi sanin matsalolinsu ta yadda za su magance su.

Sai dai wasu na ganin su ma suna da nasu laifukan wadanda ke da alaka da zargin cin hanci da rashawa, ko da yake sun sha musantawa.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp