fidelitybank

Gwamnoni ne za su ke ciyar da Fursunoni – Gwamnati

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, za ta daina ciyar da fursunonin jihohi da ke tsare a gidajen yarin ƙasar daga ƙarshen wannan shekara.

Ta shawarci jihohin ƙasar su yi cikakken amfani da gyaran fuskar da aka yi wa tsarin mulkin Najeriya a baya-bayan nan, don kyautata rayuwar fursunoninsu.

Wata sanarwa daga ma’aikatar cikin gida, ta ambato Ministan cikin gida, Rauf Aregbesola na cewa matakin, zai fara aiki ne daga ranar 31 ga watan Disamban 2023.

Ya yi shelar cewa Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannu a kan dokar yi wa tsarin mulkin Najeriya gyaran fuska, abin da ya cire harkar kula da gidajen yari daga ƙarƙashin ikon gwamnatin tarayya kaɗai, zuwa ƙarƙashin ikon haɗin gwiwar gwamnatin tarayya da jihohi.

Don haka in ji sanarwar ma’aikatar cikin gida “Daga ranar 1 ga watan Janairun 2024, gwamnatin tarayya za ta daina ciyar da ɗaurarrun da suka aikata laifuka a jihohi amma ake tsare da su a gidajen yarin tarayya.

Jazaman ne kuma, jihohi su fara yin kasafin kuɗi don ciyar da ɗaurarrunsu da ke gidajen yarin tarayya a daidai lokacin da muke jiran su gina gidajen yari na kansu.”

Ya ce matakin zai taimaka wajen ƙara rage cunkoso a gidajen yarin Najeriya.

Ministan ya ce mutanen da suka aikata laifi a jihohi ne fiye da kashi 90% na ɗaurarrun da ke gidajen yarin Najeriya a yanzu.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp