fidelitybank

Gwamnoni na sace kudaden kananan hukumomi – Buhari

Date:

Shugaba Muhammadu Buhari, ya ce, gwamanonin jihohin kasar nan na sace kason kudaden da ake tura wa kananan hukumomi duk wata daga asusun tarayya.

Shugaban ya yi wannan zargi ne a taron manyan jami’an gwamnati na wannan shekara, na cibiyar nazarin manufofi da dabaru ta kasa (NIPSS) da ke Kuru, a Jos.

A duk shekara dai masu yin kwas a cibiyar, sukan  dauki wani muhimmin lamari da ya shafi kasa baki daya, su yi nazari game da shi, kuma a karshe su gabatar da sakamakon bincikensu da shawarwarinsu.

A bana sun duba batun mulkin kananan hukumomi ne bayan da Shugaban ya ba su umurnin gudanar da nazari a kan yadda ake gudanar da mulkin kananan hukumomi.

Mai  magana da yawun shugaban kasar,  Mallam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa manyan jami’an gwamnatin sun kammala aikin nasu kuma sun bayar da shawarwari:

“ Muhimmai a ciki sun hada da rashin tsari na dimukraddiya”

Shugaba Buhari ya ce a yanzu haka jihohi 20 ne kawai suke da zababbun shugabannin kananan hukumomi  da jama’a suka zaba.

Ya ce wasu mulki ake yi  a karkashin kantoma wanda ba zababbe ba ne kamar yadda Garba Shehu ya bayyana.

”Wuraren da aka zabi shugabannin kananan hukumomi ba lallai ne a ce an rungumi al’umma na kananan hukumomin ana tafiya da su ba.” Kamar yaddaya ce.

”Akwai rashawa da cin hanci, akwai kuma rashin fahimtar aiki, akwai rashin kwarewa na ma’aikata, akwai rashin kudi da za a yi aiki da shi” in ji shi.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp