fidelitybank

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Date:

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su fifita walwalar ƴan Najeriya ta hanyar zuba jari a ƙauyuka da yankunan karkara, ta hanyar bunƙasa wutar lantarki da ayyukan noma domin kawar da talauci.

Kiran na zuwa ne bayan gabatar da wani shirin gwamnati na musamman kan bunƙasa tattalin arziki a matakin mazaɓu da aka yi wa laƙabi da ‘Renewed Hope Ward Development Programme (RHWDP)’ da ministan kasafi da tsare-tsare na ƙasar ya yi a lokacin taron majalisar tattalin arzikin ƙasar.

Manufar sabon shirin na RHWDP shi ne tabbatar da bunƙasar tattalin arziki ta hanyar taimaka wa mazaɓun ƙasar 8,809 a faɗin jihohin ƙasar 36, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasar ta bayyana.

Shugaba Tinubu ya kuma buƙaci gwamnonin ƙasar su yi duk mai yiwuwa wajen tallafa wa rayukan ƴan ƙasar daga tushe.

”Ina kira a gare ku, mu ƙara ƙaimi wajen sauya halin da mutanenmu ke ciki a yankunan karkara”, in ji Tinubu, kamar yadda sanarwar ta ambato.

“Tsare-tsaren tattalin arzikinmu na tafiya yadda ya kamata. Mun kama hanyar farfaɗowa, amma muna buƙatar ƙara ƙaimi a yankunan karkara. Mun san halin da ƙauyukanmu ke ciki, don haka mu haɗa hannu wajen yin abin da zai tallafa musu,” in ji shi.

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp