fidelitybank

Gwamnoni ku mayar da hankali a kan noma – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya jaddada muhimmancin gwamnonin jihohi wajen samar da cigaba da wadata a Najeriya, inda ya ce jagorancinsu a matakin jihohi ya zama babbar hanyar cimma burin samun wadatar abinci, bunkasar tattalin arziki, da saurin cigaban kasa.

Shugaban ya bayyana haka ne yayin wata ziyara da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, da Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) suka kai masa a gidansa da ke Ikoyi, Shugaban ya nuna godiya ga goyon baya da hadin kan da suke bayarwa tare da yin nuni ga muhimman fannoni da ke bukatar aiki tare domin cigaban kasa.

“Ku ne mafi muhimmanci wajen wadata da cigaban Najeriya. Gwamnatin Tarayya tana da kusan kashi 30 zuwa 35 cikin 100 na kudaden da ake raba wa; sauran duk yana zuwa gare ku. Silsilar darajar aikin gona na hannunku ne. Kuna da filaye, aikin kuma yana hannunku,” in ji shi.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Bayo Onanuga, Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa ya sanya wa hannu a ranar Laraba.

“Shugaban Kasa Tinubu ya bukaci karin hadin kai tsakanin gwamnatin tarayya da jihohi domin magance manyan kalubale, ciki har da ‘yancin kan kananan hukumomi, bunkasar aikin gona, da daidaituwar kudin kasa,” sanarwar ta bayyana.

Shugaban Kasa ya kuma jaddada kudurinsa na bunkasa ci gaban kananan hukumomi da ‘yancin kai, yana mai cewa wannan muhimmi ne don ci gaban karkara, yana kuma karyata jita-jitar samun sabani da gwamnonin.

“Akwai jita-jitar cewa mun samu sabani kan ‘yancin kan kananan hukumomi. A’a. Ku dai jagoranci cigaban kananan hukumomi. Babu wanda yake son karbe su daga gare ku, amma muna bukatar hadin kai. Mu yi hakan tare mu tabbatar Najeriya ta samu cigaba.”

Shugaban Tinubu ya bukaci gwamnonin su fifita cigaban aikin gona a matsayin wata hanya ta samun cigaban tattalin arziki.

Ya kuma yabawa kokarin gwamnonin yana mai cewa babu wata jiha da ba za a iya ziyarta ba don alfahari da ci gabanta:

“Babu wata jiha da ba za mu iya ziyarta ba mu yi alfahari da cigabanta. Muna samun karin kudade yanzu. Ku bar ni na dauki zagi ku kuma ku karbi yabon. Tare za mu gina kasa da za mu yi alfahari da ita,” in ji shi.

Da yake tunawa da tafiyar shugabancinsa a watanni 19 da suka gabata, Shugaban ya nuna kwarin guiwa kan damar Najeriya ta ci gaba idan aka yi la’akari da jajircewar da jagorancin gwamnatinsa ke nunawa.

Shugaban Tinubu ya nuna farin ciki kan bayyana shi da jaridar ThisDAY a matsayin gwarzon Shekara.

Ya yabawa jaridar kan gane muhimmancin abin da suka fara dauka a matsayin gazawa, amma yanzu nasara ce.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp