Gwamnonin jihohin kasar nan 36 sun daukaka kara kan hukuncin da kotu ta yanke na kalubalantar shirin cire dala miliyan 418 daga asusun tarayya.
Ana nufin kudin ne domin a warware basussukan da ake bin masu ba da shawara da gwamnatocin jahohi da na kananan hukumomi suka yi a kan maido da kudin Paris Club.
A ranar 25 ga watan Maris ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta yi watsi da karar da manyan lauyoyin jihohin kasar 36 suka shigar inda suke kalubalantar shirin gwamnatin tarayya na cire kudade daga asusun tarayya na biyan bashin dala miliyan 418 na shari’a dangane da kudaden Paris Club.
Gwamnonin sun yi wannan roko ne ta hannun babban Lauyan su a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun manyan Lauyoyin Najeriya biyar, S.I. Ameh, J. S. Okutepa, Dr Garba Tetengi, Ahmed Raji da Olumuyiwa Akinboro.
Gwamnonin sun shawarci jama’a da duk wasu cibiyoyin kudi a Najeriya da kuma kasashen waje cewa, lamarin na karkashin kasa ne, inda suka bukace su da su daina hulda da wadanda ake tuhuma a cikin karar kudin. A cewar PM News.