fidelitybank

Gwamnatin Zamfara ta rufe kafofin yada labarai 6

Date:

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ba da umarnin rufe kafofin yaɗa labarai shida saboda zargin saɓa dokokin da gwamnatin ta kafa.

Kwamashinan Yaɗa Labarai Ibrahim Dosara ya faɗa wa BBC Hausa cewa an rufe su ne saboda sun yaɗa taron jam’iyyar adawa ta PDP duk da cewa gwamnatin jihar ta hana tarukan siyasa saboda dalilai na tsaro.

Ya ce Majalisar Tsaro ta Zamfara ce ta amince tare da ba da umarnin rufe gidajen labaran da suka ƙunshi Radio Najeriya, da Pride FM Gusau, da NTA Gusau, da Gamji Talabijin, da Vision FM, da Al Umma TV.

Sai dai jam’iyyar PDP a jihar ta musanta zargin karya dokar, tana mai cewa hukumar kula da kafofin yaɗa labarai ta ƙasa, NBC, ce kaɗai ke da ikon rufe kafofin.

A kwamashinan, majalisar ta kuma umarci kwamashinan ‘yan sanda da ya kama dukkan ‘yan jaridar da suka halarci taron wanda ɗan takarar gwamna na PDP, Dauda Lawal Dare, ya shirya.

Tun farko gwamnatin Zamfara ta ba da sanarwar hana tarukan siyasa tare da ɗaukar matakan tsaro na musamman a ƙananan hukumomin Anka da Gusau da Gumi da Bukuyum – inda hare-haren ‘yan fashin daji suka fi ƙamari.

Sai dai PDP ta shirya taron a ranar Asabar da zimmar karɓar wasu ‘yan adawa da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar tasu, har ma rahotanni suka ce an samu hatsaniya tsakaninsu da ‘yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp