Gwamnatin Jihar Zamfara ta ba da umarnin rufe kafofin yaɗa labarai shida saboda zargin saɓa dokokin da gwamnatin ta kafa.
Kwamashinan Yaɗa Labarai Ibrahim Dosara ya faɗa wa BBC Hausa cewa an rufe su ne saboda sun yaɗa taron jam’iyyar adawa ta PDP duk da cewa gwamnatin jihar ta hana tarukan siyasa saboda dalilai na tsaro.
Ya ce Majalisar Tsaro ta Zamfara ce ta amince tare da ba da umarnin rufe gidajen labaran da suka ƙunshi Radio Najeriya, da Pride FM Gusau, da NTA Gusau, da Gamji Talabijin, da Vision FM, da Al Umma TV.
Sai dai jam’iyyar PDP a jihar ta musanta zargin karya dokar, tana mai cewa hukumar kula da kafofin yaɗa labarai ta ƙasa, NBC, ce kaɗai ke da ikon rufe kafofin.
A kwamashinan, majalisar ta kuma umarci kwamashinan ‘yan sanda da ya kama dukkan ‘yan jaridar da suka halarci taron wanda ɗan takarar gwamna na PDP, Dauda Lawal Dare, ya shirya.
Tun farko gwamnatin Zamfara ta ba da sanarwar hana tarukan siyasa tare da ɗaukar matakan tsaro na musamman a ƙananan hukumomin Anka da Gusau da Gumi da Bukuyum – inda hare-haren ‘yan fashin daji suka fi ƙamari.
Sai dai PDP ta shirya taron a ranar Asabar da zimmar karɓar wasu ‘yan adawa da suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar tasu, har ma rahotanni suka ce an samu hatsaniya tsakaninsu da ‘yan jam’iyyar APC mai mulkin jihar.