Ma’aikatar kananan hukumomi da masarautu ta jihar Zamfara ta dakatar da Hakimin Sabon Garin da ke Gusau, Haliru Magajin Sabon Garin.
Matakin dai ya biyo bayan wani kwakkwaran bincike da aka gudanar kan zargin da ba a bayyana ba a kan basaraken.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban mai ba da shawara na musamman kan harkokin masarautu, Hon. Bello Aliyu Acha.
A cewar sanarwar, dakatarwar ya yi daidai da kudurin gwamnatin jihar na tabbatar da adalci da gaskiya, tare da tabbatar da cewa shugabanni a cikin al’ummomi na bin tsarin da’a.
Sanarwar ta ce “Ma’aikatar za ta gudanar da cikakken bincike don gano gaskiyar zargin da ake yi masa.”
Ya kuma bayyana cewa za a dauki matakai ne bisa sakamakon binciken.