Ma’aikatar noma ta kasa ta ce, za ta gina ɗakunan gwaje-gwajen nau’o’in ƙasa a ƙananan hukumomin jihar Kano 44.
Ma’aikatar ta ce ɗakunan binciken za su taimaka wa manoma wajen tantance irin shukar da ta dace da ƙasar gonakinsu ta yadda za a samu yabanya.
Ƙarƙashin shirin an zaɓi jihohin Kano da Oyo don yin gwaji, inda ake fatan samar da na’urorin zamani da ƙwararrun ma’aikata.
Alhaji Isa Isayaku Hotoro babban jami’i a ma’aikatar harkokin noma da bunƙasa samar da abinci ta tarayya da ke jihar Kano shi ne ya wakilci ministan ma’aikatar a wajen wani taron tattaunawa game da yadda za a samar da ɗakunan a Kano.