fidelitybank

Gwamnatin Tinubu ta ayyana dokar ta ɓace a kan matsalar wutar lantarkin Arewa – Ƙungiyar Dattawan Arewa

Date:

Kungiyar tuntubar juna ta dattawan Arewacin ƙasar nan ACF, ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ayyana dokar ta-ɓaci kan ɓangaren wutar lantarki a daidai lokacin da yankin arewacin ƙasar ke ci gaba da kasancewa cikin duhu sakamakon rashin wuta.

Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na ƙasa na ƙungiyar, Tukur Muhammad-Baba ya fitar, ta yi zargin cewa dagan-gan gwamnati ta banzatar da harkar lantarki a yankin domin ƙara jefa harkokin kasuwanci cikin matsi.

ACF ta bayyana mamakin cewa me ya sa arewa wadda ke samar da wutar lantarki mai yawa a ƙasar, amma kuma a ke kasawa a ba ta kaɗan.

“Cikin mako ɗaya da ya gabata, sassan jihohin arewacin Najeriya da dama na fuskantar matsalar rashin wutar lantarki, abin da ya janyo harkokin kasuwanci da na yau da kullum suka kusa durkushewa, ga kuma ƙaruwar ɓacin-rai tsakanin al’umma,” in ji ƙungiyar.

ACF ta ce abin yana tayar da hankali matuka duba da irin sanarwa da kamfanin rarraba wutar lantarki a Najeriya (TCN) ya fitar cewa za a ci gaba da fuskantar matsalar saboda matsalolin tsaro da ake fama da su.

Ta ce bai kamata a ce jihar Legas kaɗai tana da ƙananan tashoshin samar da lantarki har guda takwas ba yayin da ɗaukacin jihohin arewa, waɗanda ke da sama da rabin al’ummar Najeriya ke da tashoshi guda uku kaɗai a Jos da Kaduna da kuma Kano.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa lamarin babbar barazana ce ga tsaron ƙasar.

Don haka ta yi kira ga gwamnatin tarayya da sauran hukumomi da abin ya shafa da su gaggauta ayyana dokar ta-ɓaci kan matslar ta rashin lantarki, kafin matsalar ra rikiɗe zuwa tashin hankali.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp