fidelitybank

Gwamnatin Tinubu na sane da ‘yancin ‘yan Najeriya na yin zanga-zanga – Minista

Date:

Ministan yaɗa labarai Mohammed Idris, ya ce, a daidai lokacin da gwamnatin Shugaba Tinubu ke martaba ƴancin ƴanƙasa na gudanar da zanga-zangar lumana, gwamnatin ta ƙudiri aniyar hakan bai take haƙƙin sauran ‘yanƙasa ba.

Mohammed Idris ya ce suna da bayanan da ke nuna cewa wasu ɓata-gari na da niyyar fakewa da zanga-zangar wajen tayar da fitina.

“Shugaban ƙasa ba shi adawa da zanga-zanga, kawai dai yana ƙin tashin hankali da kuma duk wani abu da zai tauye walwalar ‘yan Najeriya,” a cewarsa lokacin da yake karɓar baƙuncin ƙungiyar bishop-bishop ta Charismatic Bishop Conference a ofishinsa da ke Abuja yau Laraba.

“Ya yarda cewa kowa na da ‘yancin yin duk wani abu da bai saɓa doka ba kamar yadda dimokuraɗiyya ta tanada matuƙar dai ba a tauye wa wani haƙƙinsa ba.”

A jiya Sufeto Janar na ‘Yansanda Kayode Egbetokun ya ce za su bai wa masu zanga-zangar kariya “matuƙar dai ta lumana ce”, amma ba za su bari “mutane su ƙona gine-gine ba da sunan zanga-zanga”.

Matasa a Najeriya na cigaba da tattauna batun zanga-zangar da suke cewa za a fara daga 1 ga watan Agusta domin nuna fushinsu game da tsadar rayuwa da ake fama da ita a ƙasar.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp