fidelitybank

Gwamnatin Tarayya za ta kaddamar da noman rani a Jigawa

Date:

Gwamnatin tarayya za ta kaddamar da noman rani na wannan shekara a Hadejia da ke jihar Jigawa.

Cikin wata sanarwa da ma’aikatar albarkatun noma da samar da abinci ta kasa, ta fitar ta ce mataki wani bangare ne na kokarin kawar da tsadar abinci a fadin kasar.

A cikin watan Yuli ne shugaban kasar Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-baci kan samar da abinci a fadin Najeriya.

Ministan harkokin noma da samar da abinci na kasar Sanata Abubakar Kyari ne zai jagoranci masu ruwa da tsaki zuwa garin Hadejia a jihar Jigawa domin kaddamar da aikin a ranar Asabar 25 ga watan Nuwamba, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Sanarwar ta ce za a bai wa manoma kayyakin aikin noma da suka kunshi iri da takin zamani da magungunan feshi a lokacin bikin.

Tuni dai gwamnatin kasar ta ce ta yi rangwamen kayayyakin aikin noma da kashi 50

Ana sa ran gudanar da noman ranin a duka jihohin kasar 36 da Abuja.

Inda ake ra san shuka alkamar – da aka shigo da irinta daga Mexico – da shinkafa, da masara da dawa da waken suya da kuma rogo.

Kamfanonin sarrafa fulawa hudu ne suka bayyana aniyarsu na sayen alkamar daga wajen manoman.

Ministan albarkatun noman ya bayyana kaddamar da shirin da cewa wani gagarumin ci gaba, a yunkurin da gwamnatin kasar ke yi na burin inganta kasar.

Ya kara da cewa samar da kayayyakin aikin noma da na’urorin zamani za su taimaka wajen habaka harkokin noma a fadin Najeriya.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp