Gwamnatin tarayya ta amince da sabbin makarantun Kwalejin Fasaha uku na gwamnatin tarayya, a wani bangare na kokarin ganin an samu saukin karatun manyan makarantu a kasar nan.
Za a gina makarantun ne a Umunnoechi, jihar Abia, jihar Orogun Delta, da kuma Kabo a jihar Kano.
A cewar sanarwar da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar ilimi ta tarayya Ben Bem Goong ya fitar, sabbin cibiyoyin za su fara ayyukan ilimi ne a watan Oktoban 2022.
Wannan ya kawo adadin makarantun Kwalejin Fasaha a kasar nan sun kai 36.
Duk jihohin tarayyar yanzu suna da Kwalejin Fasaha kowace.