Gwamnatin tarayya ta ce, kowane dan Najeriya da ya dawo daga kasar Ukraine zai samu dala 100 idan ya isa filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe dake Abuja.
A safiyar Juma’a ne jirgin Air Peace ya fara kwashe ‘yan Najeriya da suka tsere daga Ukraine ta Poland.
Kimanin ‘yan Najeriya 2,000 ne aka ce sun tsere daga kasar Ukraine a lokacin da Rasha ta mamaye kasar.
A ranar Laraba ne gwamnatin tarayya ta amince da dala miliyan 8.5 domin kwashe ‘yan Najeriya da suka makale a yakin Rasha da Ukraine.
A cewar Karamin Ministan Harkokin Waje, Zubairu Dada, kasashen da za a fara jigilar jirage sun hada da Poland, Hungary, Slovakia, da Romania.
Jirage biyu daga Air Peace da daya daga Max Air za su gudanar da aikin kwashe mutanen.