Al’ummar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna, sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta faɗaɗa shirin sasanci da ƴanbindiga da aka yi a yankin zuwa sauran jihohin da ke fama da matsalolin rashin tsaro.
Wannan kiran na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ci gaban yankin masarautar Birnin Gwari wato Birnin Gwari Birnin Gwari Emirate Progressives Union (BEPU), wadda shugabanta Isah Muhammad ya sanya wa hannu.
Sanarwar ta ce al’ummar yankin suna godiya da zaman lafiya da suka fara samu a sanadiyar sasancin, “amma muna kira da a faɗaɗa shirin zuwa sauran jihohin da suke fama da matsalar ƴanbindiga irin su Neja da Zamfara da Katsina da Sokoto domin hakan ne zai wanzar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.”
Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jiha da su samar da ababen more rayuwa a yankin na Birnin Gwari, “akwai buƙatar a gyara titin Birnin Gwari zuwa Kaduna da na zuwa Funtua da zuwa Neja da na zuwa Tegina, wanda ya sada yankin da kudancin Najeriya.”
BEPU ta kuma kira ga kamfanonin sadarwa irin su MTN da Airtel da su dawo da hanyoyin sadarwarsu da suka katse a baya a yankin, sannan ƙungiyar ta yi kira a kafa jami’ar nazarin ayyukan noma saboda yadda ake noma a yankin.
Yankin Birnin Gwari ya daɗe yana fama da matsalar tsaro, amma cikin ƴan kwanakin nan an fara samun zaman lafiya, inda harkokin kasuwanci da noma suka fara komawa yadda ya kamata bayan wani shirin sasanci da ƴanbindiga da gwamnatin ta jagoranta.