fidelitybank

Gwamnatin tarayya ta yi sulhu da ƴan Bindiga – Mazauna Birnin Gwari

Date:

Al’ummar Birnin Gwari da ke jihar Kaduna, sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta faɗaɗa shirin sasanci da ƴanbindiga da aka yi a yankin zuwa sauran jihohin da ke fama da matsalolin rashin tsaro.

Wannan kiran na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da ƙungiyar ci gaban yankin masarautar Birnin Gwari wato Birnin Gwari Birnin Gwari Emirate Progressives Union (BEPU), wadda shugabanta Isah Muhammad ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta ce al’ummar yankin suna godiya da zaman lafiya da suka fara samu a sanadiyar sasancin, “amma muna kira da a faɗaɗa shirin zuwa sauran jihohin da suke fama da matsalar ƴanbindiga irin su Neja da Zamfara da Katsina da Sokoto domin hakan ne zai wanzar da zaman lafiya a faɗin ƙasar.”

Sanarwar ta kuma yi kira ga gwamnatin tarayya da ta jiha da su samar da ababen more rayuwa a yankin na Birnin Gwari, “akwai buƙatar a gyara titin Birnin Gwari zuwa Kaduna da na zuwa Funtua da zuwa Neja da na zuwa Tegina, wanda ya sada yankin da kudancin Najeriya.”

BEPU ta kuma kira ga kamfanonin sadarwa irin su MTN da Airtel da su dawo da hanyoyin sadarwarsu da suka katse a baya a yankin, sannan ƙungiyar ta yi kira a kafa jami’ar nazarin ayyukan noma saboda yadda ake noma a yankin.

Yankin Birnin Gwari ya daɗe yana fama da matsalar tsaro, amma cikin ƴan kwanakin nan an fara samun zaman lafiya, inda harkokin kasuwanci da noma suka fara komawa yadda ya kamata bayan wani shirin sasanci da ƴanbindiga da gwamnatin ta jagoranta.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp