fidelitybank

Gwamnatin tarayya ta yi ayyuka sama da 50 a jiha ta – Orji Kalu

Date:

Bulaliyar majalisar dattijai, Orji Uzor Kalu, ya bayyana cewa gwamnati tarayya ta yi ayyukan hanyoyi sama da 50 a fadin jihar Abia Ta Arewa.

Da ya ke magana a ranar Litinin a wajen bikin Ezumezu na kabilar Igbere, a karamar hukumar Bende, tsohon gwamnan Abia, ya ce ayyukan da a ke gudanarwa sun nuna cewa gwamnatin APC na gudanar da ayyukanta.

Ya jaddada cewa kammala wasu hanyoyin zai kawo tallafi ga masu amfani da hanyar a yankin.

A cewar Kalu, ayyukan da a ka yi a gundumar Sanata ta Abia ta Arewa sun kasance mafi girma a daukacin shiyyar Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu.

Ya kara da cewa, an yi watsi da wasu hanyoyi da gadoji tun shekaru biyar zuwa sittin da suka gabata, inda ya ce,”Kashi 68% na kuri’un da jam’iyyar APC mai mulki ta baiwa jam’iyyar APC a zaben da ya gabata ba asara ba ne”.

Ya yi kira ga Gwamna Okezie Ikpeazu da ya sa baki a hanyar Uzoakoli- Igbere-Abiriba-Ohafia da ta gaza wadda hanya ce ta jihar. A cewarsa, ya ware Naira biliyan 1, domin sake gina hanyar.

“Ina so in bayyanawa Ndi Igbere a fili, musamman hanyar Uzuakoli ba mallakin gwamnatin tarayyar Najeriya ba ne, na sanya Naira biliyan 1 a wurin, domin yin titin, duk da cewa ba su yi ba a yanzu, saboda hanyar ta Abia ce. gwamnatin jiha kuma ina kira ga gwamnan jihar Abia da ya sake duba waccan hanyar, a lokacin da na ke gwamna, waccan hanyar ba a jihar nan take ba, ina yin ta ne saboda mun yi amfani da ita, ina so in roki Dr. Okezie Ikpazu, ba wai cikin rigima ba, amma muna rokonsa domin Allah ya sami tagomashi a ransa ya ba mu wannan hanyar, hanya ce ta mu.

“A cikin kasafin kudin 2021, biliyan daya na kan wannan hanya kamar yadda majalisar dattawa ta ware, amma ma’aikatar ayyuka na tafiyar hawainiya, saboda ba mallakin gwamnatin tarayyar Najeriya ba ne”.  A cewar Sanata Orji Kalu.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp