Gwamna Samuel Ortom na jihar Benuwe, ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta saki shugaban kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, Nnamdi Kanu a wani bangare na kokarin samar da zaman lafiya a kasar.
Gwamnan ya lura cewa batun Kanu kalubale ne na zamantakewa da siyasa wanda ya kamata a magance shi a siyasance. In ji Vanguard.
A cewar wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin kasashen waje, Peter Ichull, gwamnan ya yi wannan kiran a jiya a lokacin da wata kungiya karkashin kungiyar tsoffin sojojin Amurka ‘yan kabilar Igbo suka kai masa ziyarar ban girma a birnin Washington DC na kasar Amurka.