Hukumar kashe gobara ta tarayya, ta amince da karin girma ga jamiāan hukumar kashe gobara (FFS) 2,382.
ACF Paul Abraham, kakakin hukumar ta FFS ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba.
A cewar sanarwar, Konturola Janar na FFS, Engr Jaji Abdulganiyu ne ya sanar da karin girma da ci gaban ta cikin wata sanarwa ta cikin gida.
Ya ce, an kara wa jamiāai 363 karin girma yayin da 2,019 suka samu karin girma daga matsayin mataimakan Sufurtandanda na kashe gobara (ASF I) da mataimakin Sufurtandan kashe gobara (DSF) a shekarar 2022.
Jaji ya yabawa ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola, wanda shi ma ya zama shugaban hukumar, da sauran mambobi bisa irin rawar da suka taka wajen inganta jamiāan sa.
Ya taya daukacin sabbin jamiāan da aka samu karin girma da kuma manyan jamiāai murna, sannan ya bukace su da su yi iya kokarinsu wajen tabbatar da karin girma/ci gaba.
Jaji ya umurci shuwagabannin kwamandoji da sassan da su yi wa dukkan jamiāan ado a cikin umarninsu da sassansu.