fidelitybank

Gwamnatin Tarayya ta kafa kwamiti a kan baiwa ƙananan hukumomi hakkin su

Date:

Gwamnati ta ƙaddamar da wani kwamiti mai mutum 10 da zai duba shirin aiwatar da hukuncin da Kotun Ƙolin ƙasar ta yi game da bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin gashin-kai.

A ranar 11 ga watan Yulin da ya gabata ne Kotun Ƙolin ta yanken hukuncin cewa matakin da gwamnonin jihohi ke ɗauka na ci gaba da riƙe wa ƙananan hukumomi kuɗaɗen gudanarwasu ya saba wa doka.

Makonni biyu da yanke wannan hukuncin Sakataren Gwamnati Sanata George Akume, ya kafa kwamitin domin aiwatar da wannan hukuncin.

Kwamitin da ya ƙunshi ministan kuɗi da babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a da ministan kasafin kudi da tsare-tsare, da babban akanta kuɗi na ƙasa da gwamnan babban bankin Najeriya da babban sakatare a ma’aikatar kuɗi da tara haraji da wakilan gwamnonin jahohi da kuma na kananan hukumomi.

Darakta watsa labarai na ofishin sakataren gwamnatin tarayyar Najeriya, Segun Imohiosen, ya bayyana cewa babban muradin da kwamitin ya sanya a gaba shi ne tabbatar da an bai wa duka ƙananan hukomi 774 na ƙasar, ‘yancin gashin kai, ta yadda za su yi amfani da kuɗinsu ba tare da fuskantar katsalandan daga gwamnonin jahohi ba, kamar yadda shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya saka wa muradin ganin an bi turbar da kundin tsarin mulkin Najeriya ya sharɗanta.

A tsarin rabon tattalin arziki da kuɗaɗen gudanarwar wata-wata gwamnatin tarayya na samun kashi 52.68 cikin 100, jihohi masu kashi 26.72, yayin da ƙananan hukumomi ke samun kashi 20.60 cikin 100 na kuɗin.

Masana dai na ganin za a samu sauyi ga bunƙasar ƙananan hukumomi musamman idan har suna da damar tafiyar da kuɗaɗensu, muddin babu wata hanya ta zangon-ƙasa da aka bijiro da ita, kasancewar kuma su ne suka fi kusa da talakawa.

Sai dai duk hasashen samun sauyin bayan hukuncin Kotun Ƙolin, wasu na bayyana shakku kan yadda za a tabbatar ba a yi facaka da kuɗaɗen ba kamar yadda aka yi a baya ba.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp