fidelitybank

Gwamnatin Tarayya ta gargaɗi Obi da ya shiga taitayinsa

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, cin amanar kasa ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, LP, Peter Obi, ya tunzura mutane zuwa tashin hankali sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ministan yada labarai da al’adu Lai Mohammed ne ya bayyana haka a birnin Washington DC a lokacin da yake ganawa da kungiyoyin yada labarai na duniya.

NAN ta ruwaito cewa, Mohammed ya zuwa yanzu yana mu’amala da kafafen yada labarai kamar Washington Post, Muryar Amurka, Associated Press da Mujallar manufofin kasashen waje.

A daya daga cikin mu’amalar da aka yi, ministan ya ce, ba daidai ba ne Obi ya nemi a yi masa hukunci a kotu kan sakamakon zaben da kuma tada zaune tsaye.

“Obi da mataimakinsa, Datti Ahmed, ba za su iya yi wa ‘yan Najeriya barazana cewa idan aka rantsar da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu na jam’iyyar APC a ranar 29 ga watan Mayu, zai kawo karshen mulkin dimokuradiyya a Najeriya.

“Wannan cin amana ne. Ba za ku iya zama kuna gayyatar tayar da hankali ba, kuma abin da suke yi ke nan.

“Maganar Obi na mutum ne mai yanke kauna, ba shi ne dan dimokradiyya da ya yi ikrarin zama ba.

“Bai kamata dan dimokradiyya ya yi imani da dimokradiyya ba kawai idan ya ci zabe,” in ji Mohammed.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp