fidelitybank

Gwamnatin Tarayya ta gargaɗi Obi da ya shiga taitayinsa

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, cin amanar kasa ne dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, LP, Peter Obi, ya tunzura mutane zuwa tashin hankali sakamakon zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

Ministan yada labarai da al’adu Lai Mohammed ne ya bayyana haka a birnin Washington DC a lokacin da yake ganawa da kungiyoyin yada labarai na duniya.

NAN ta ruwaito cewa, Mohammed ya zuwa yanzu yana mu’amala da kafafen yada labarai kamar Washington Post, Muryar Amurka, Associated Press da Mujallar manufofin kasashen waje.

A daya daga cikin mu’amalar da aka yi, ministan ya ce, ba daidai ba ne Obi ya nemi a yi masa hukunci a kotu kan sakamakon zaben da kuma tada zaune tsaye.

“Obi da mataimakinsa, Datti Ahmed, ba za su iya yi wa ‘yan Najeriya barazana cewa idan aka rantsar da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu na jam’iyyar APC a ranar 29 ga watan Mayu, zai kawo karshen mulkin dimokuradiyya a Najeriya.

“Wannan cin amana ne. Ba za ku iya zama kuna gayyatar tayar da hankali ba, kuma abin da suke yi ke nan.

“Maganar Obi na mutum ne mai yanke kauna, ba shi ne dan dimokradiyya da ya yi ikrarin zama ba.

“Bai kamata dan dimokradiyya ya yi imani da dimokradiyya ba kawai idan ya ci zabe,” in ji Mohammed.

latest news in nigeria today 
2021 ripples

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp