fidelitybank

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da karatun digiri na jamhuriyar Benin da Togo

Date:

Najeriya ta ce ta ɗauki matakin dakatar da tantance shaidar karatun digiri daga jami’o’in Jamhuriyar Benin da na Togo.

Matakin ya zo ne bayan wani rahoton binciken ƙwaƙwaf da jaridar Daily Nigerian ta yi a baya-bayan nan, inda ta ce wani wakilinta da ya ɓad-da-kama ya samu takardar shaidar digiri daga wata jami’a a Jamhuriyar Benin a cikin mako shida kacal.

Mai magana da yawun ma’aikatar ilimi ta Najeriya, Augustina Obilor-Duru cikin wata sanarwa da ta fitar, na cewa rahoton ya bayyana hanyoyin da wasu ƴan Najeriya ke bi domin samun takardar shaidar karatun digiri da nufin samun damamrmakin aiki da ba su cancanta ba.

“Ma’aikatar ilimi ta koka da irin wannan ɗabi’a kuma daga ranar 2 ga watan Janairun 2024, ta dakatar da tantance takardun shaidar karatun digiri daga Benin da Togo har zuwa lokacin da za a kammala bincike.

“Binciken dai zai haɗar da ma’aikatar harkokin waje ta Najeriya da kuma ƙasashen biyu da ma’aikatun da ke kula da ilimi a ƙasashen da kuma hukumar tsaro ta farin kaya da hukumar kula da shirin matasa ‘yan hidimar ƙasa, NYSC.”

Ma’aikatar ta yi kira ga yan Najeriya su ba da gudunmawa wajen samar da bayanan da za su taimaka wa kwamitin yayin da yake neman hanyoyin magance faruwar haka a gaba.

Ma’aikatar ta kuma yi bayani kan ƙalubalen da take fuskanta game da matsalar bara-gurbin makarantun ƙetare ko a cikin gida waɗanda mutanen da ba su ji ba su gani ba, ke faɗawa tarkonsu ko kuma wasu ƴan Najeriya waɗanda da saninsu suke karatu a makarantun.

Ma’aikatar ilimin ta ce za ta ci gaba da nazari domin toshe duk wata kafa da hanyoyi da tsare-tsare tare da ladabtar da jami’an da ke da hannu a irin wannan lamari.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp