fidelitybank

Gwamnatin Tarayya ta dakatar da bayar da kudin kananan hukumomin jihar Rivers

Date:

Gwamnatin Tarayya ta tabbatar da cewa, ta dakatar da kwamitin raba asusun tarayya na watan Oktoba, biyan kudaden shiga na FAAC ga jihar Ribas a dai dai lokacin da ake ci gaba da fafatawa tsakanin gwamna Simi Fubara da ministan babban birnin tarayya, Nyesome Wike.

Kakakin ofishin Akanta Janar na kasa Bawa Mokwa ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a.

Hakan na zuwa ne a yayin da gwamnatin Najeriya a ranar Larabar da ta gabata ta sanar da amincewa da fitar da naira tiriliyan 1.1411 a matsayin kudaden rarar kudaden shiga na asusun tarayya na watan Oktoba na shekarar 2024 ga majalisun tarayya, jihohi, da kananan hukumomi.

Sai dai wani rahoto ya bayyana cewa ba a raba kudaden shigar FAAC a watan Oktoba ga jihar Ribas sakamakon wata kotu da ta dakatar da babban bankin Najeriya da gwamnatin Najeriya aiwatar da irin wannan mataki.

Da yake mayar da martani kan lamarin, Mokwa ya ce OAGF a matsayin hukumar gwamnati za ta mutunta umarnin kotu.

A halin da ake ciki, ya bayyana cewa, ba a raba kudaden shiga na FAAC na wata-wata ga jihohi ba har zuwa lokacin gabatar da rahoton.

“Abin da na samu shi ne cewa ba a rarraba FAAC na Oktoba 2024 ba tukuna. Sai dai gwamnatin tarayya za ta bi umarnin kotu kan batun rabon jihar Ribas.

“Za mu bi diddigin matakan da ya kamata muddin babu wani tsari da ya saba wa doka. Idan aka samu akasin hakan, matsayin zai kasance,” kamar yadda ya shaidawa DAILY POST.

Ya kara da cewa, “Tsarin bayar da kudade na watan Oktoba na 2024 na wata-wata yana tafiya.”

Idan za a iya tunawa, a ranar 30 ga watan Oktoba na wannan shekara mai shari’a Abdulmalik na babbar kotun tarayya ya haramtawa babban bankin Najeriya CBN da gwamnatin Najeriya ba gwamnatin jihar Ribas kudaden wata-wata.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp