fidelitybank

Gwamnatin Tarayya ta ci tarar kamfanin tabar Birtaniya dala miliyan 110

Date:

Gwamnatin tarayya ta ci tarar kamfanin taba sigari na Birtaniya mai suna British American Tobacco da sauran rassan kamfanin dala miliyan 110.

Hukumar kare haƙƙin masu sayen kaya ta Najeriya ce ta bayyana cin tarar a wata sanarwa da ta fitar, inda ta ce an ɗauki matakin ne saboda zargin keta dokar hukumar da dokar taƙaita harkokin taba sigari ta ƙasa.

Hukumar ta ƙara da cewa ya zama dole kamfanin ya mutunta dokoki sannan kuma za a riƙa bibiyar ayyukansa tsawon wata 24, kuma ya bayar da tabbaci a rubuce na kiyaye dokoki da wayar da kai game da kare lafiyar al’umma da kuma rage taba sigari.

“Domin samun masu kamfanin su cika ƙa’idoji ƙarƙashin dokar izini, hukumar ta janye tuhume-tuhumen da ake yi wa kamfanin da kuma wani ma’aikacinsa dangane da yunƙurin hana gudanar da bincike a kamfanin da kuma rashin ba da haɗin kai domin aiwatar da aikin, kamar yadda hukumar ta ce.

A cewar hukumar, ta ƙaddamar da bincike tare da ƙwace wasu kayayyaki bayan samun izinin watan babbar kotun tarayya a rassan kamfanin na BAT a ranar 25 ga watan Janairu.

Hukumar ta bayyana cewa ta tattara ta kuma samu isasshiyar hujja daga binciken ƙwaƙwaf da aka yi na kafofin sadarwa da sauran bayanai da aka tattaro sakamakon binciken da kuma shaidun da aka gano daga sahihan majiyoyi yayi da kuma bayan binciken.

Hukumar ta ƙara da cewa a shirye take ta inganta da kuma tabbatar da tsaftace kasuwanni domin kare masu sayen kayayyaki.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp