Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Juma’a, 15 ga Afrilu, da Litinin, Litinin 18 ga Afrilu, 2022 a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Easter.
Ministan harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata, ya bukaci mabiya addinin Kirista da su yi koyi da halayen sadaukarwa, hadin kai, gafara, kyautatawa, soyayya, zaman lafiya da hakuri, wadanda su ne halaye da ayyukan mabiya addinin Kiristi, kamar yadda ma’aikatarsa ta bayyana.
Ya yi kira ga mabiya addinin Kirista da sauran ‘yan Najeriya da su yi amfani da bikin Easter na bana wajen yin addu’a, domin kawo karshen duk wani kalubalen tsaro da ke addabar kowane bangare na kasar nan.
Ministan ya ba da tabbacin cewa Gwamnatin Tarayya ba za ta bar wani abu ba don ganin an kawo karshen hare-haren da wasu da ba a so suke yi a kan manyan tituna, da filin jirgin sama da na jirgin kasa a kan lokaci.