fidelitybank

Gwamnatin tarayya ta amince da sabbin manufofin magance ƙaurar likitoci

Date:

Gwamnatin tarayya ta amince da wasu sabbin manufofi da za su taimaka wa ƙasar wajen magance ƙaurar ma’aikatan lafiya zuwa wasu ƙasashe, domin rage ƙalubalen da ɓangaren lafiya na ƙasar ke fama da su.

Ministan Lafiya, Ali Pate ne ya sanar da hakan a ranar Litinin a shafin sada zumuntasa na X, yana mai jaddada ƙudurin gwamnati na magance ƙaurar ƙwararrun likitoci da ma’aikatan lafiya daga kasar.

Shugaba Bola Tinubu ne ya jagoranci zaman majalisar zartarwa ta tarayya a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda aka amince da manufar.

Najeriya na fama da yawan ƙaura da likitoci da kuma malaman jinya ke yi zuwa ƙasashen ƙetare domin neman albashi mai tsoka.

Lamarin ya jefa ɓangaren lafiya na ƙasar cikin mummunan yanayi, inda ake kokawa kan ƙarancin likitoci da sauran malaman lafiya.

“Wannan manufar an samar da ita ne ba kawai domin magance ficewar da masana kiwon lafiya ke yi zuwa ƙasashen ƙetare ba ne, har ma da aiwatar wani muhimmin tsari da zai kawo gyara a ɓangaren lafiya na ƙasar,” in ji Pate.

Ya kara da cewa manufar ta tanadi samar da ma’aikata masu inganci waɗanda za su samu tallafi mai kyau da kuma amfani da su yadda ya kamata domin biyan buƙatun kiwon lafiya na daukacin ‘yan Najeriya.

Babban makasudin sabuwar manufar ita ce karfafa dawowa da ƙwararrun likitocin Najeriya daga kasashen waje

“Wannan manufar ta kuma bayar da shawarar yin yarjejeniya da sauran ƙasashe, don tabbatar da cewa Najeriya ta amfana da musayar ma’aikatan kiwon lafiya,” in ji Ministan.

Bugu da ƙari, manufar ta jaddada mahimmancin samun daidaito a rayuwar ma’aikatan kiwon lafiya da ayyukansu na yau da kullum.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp