fidelitybank

Gwamnatin tarayya ta amince da sabbin manufofin magance ƙaurar likitoci

Date:

Gwamnatin tarayya ta amince da wasu sabbin manufofi da za su taimaka wa ƙasar wajen magance ƙaurar ma’aikatan lafiya zuwa wasu ƙasashe, domin rage ƙalubalen da ɓangaren lafiya na ƙasar ke fama da su.

Ministan Lafiya, Ali Pate ne ya sanar da hakan a ranar Litinin a shafin sada zumuntasa na X, yana mai jaddada ƙudurin gwamnati na magance ƙaurar ƙwararrun likitoci da ma’aikatan lafiya daga kasar.

Shugaba Bola Tinubu ne ya jagoranci zaman majalisar zartarwa ta tarayya a fadar shugaban kasa da ke Abuja, inda aka amince da manufar.

Najeriya na fama da yawan ƙaura da likitoci da kuma malaman jinya ke yi zuwa ƙasashen ƙetare domin neman albashi mai tsoka.

Lamarin ya jefa ɓangaren lafiya na ƙasar cikin mummunan yanayi, inda ake kokawa kan ƙarancin likitoci da sauran malaman lafiya.

“Wannan manufar an samar da ita ne ba kawai domin magance ficewar da masana kiwon lafiya ke yi zuwa ƙasashen ƙetare ba ne, har ma da aiwatar wani muhimmin tsari da zai kawo gyara a ɓangaren lafiya na ƙasar,” in ji Pate.

Ya kara da cewa manufar ta tanadi samar da ma’aikata masu inganci waɗanda za su samu tallafi mai kyau da kuma amfani da su yadda ya kamata domin biyan buƙatun kiwon lafiya na daukacin ‘yan Najeriya.

Babban makasudin sabuwar manufar ita ce karfafa dawowa da ƙwararrun likitocin Najeriya daga kasashen waje

“Wannan manufar ta kuma bayar da shawarar yin yarjejeniya da sauran ƙasashe, don tabbatar da cewa Najeriya ta amfana da musayar ma’aikatan kiwon lafiya,” in ji Ministan.

Bugu da ƙari, manufar ta jaddada mahimmancin samun daidaito a rayuwar ma’aikatan kiwon lafiya da ayyukansu na yau da kullum.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp