fidelitybank

Gwamnatin Tarayya na ƙoƙarin koyawa ɗalibai ilimin jima’i – MSSN

Date:

Ƙungiyar ɗalibai Musulmi ta Najeriya (MSSN), ta rubuta takaddar ƙorafi ga gwamnatin tarayya a kan wasu littattafai da ake koyarwa a makarantu cewa, suna ɗauke da abubuwa za su bata tarbiyya da addinin yara.

A wasikar da kungiyar shiyya ta biyu (B-Zone) ta aika wa Ministan Ilimi Adamu Adamu, ta ce wasu daga cikin littattafan na koyar da lissafi da Ingilishi da kimiyyar zamantakewa (Social Sciene) da ake amfabi da su a yawancin makarantun sakandire suna dauke da abubuwa na koyar da badala da batsa, wadanda ta ce an tsara domin an gurbata dabi’ar matasa dalibai.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, wasikar wadda ke dauke da koken babban jami’in kungiyar Qaasim da Babban Sakatarenta Abdul Jalil Abdur Razaq suka sanya wa hannu ranar 15 ga watan nan na Mayu.

Kungiyar ta MSSN ta ce wasu daga cikin littattafan na yada ilimin zubar da ciki da ludawi da madigo da amfani da kororon roba da sauran dabi’u da kungiyar ta ce ba su dace da matasa ba domin za su bata musu tarbiyya ta addini da kuma al’ada.

saboda haka kungiyar ta bukaci ma’aikatar ilimi ta Njaeriya ta gaggauta gudanar da bincike a kan dukkanin littattafan da ake amfani da su a makarantun kasar ta tabbatar ba sa dauke da abubuwan da za su bata tarbiyyar dalibai matasa.

Wasu daga cikin littattafan sun hada da: Basic Science Junior Secondary School Razat Publishers, 2018 edition, (for JSS3); New Concept English for Senior Secondary Schools for SSS2, Revised edition (2018 edition); Active Basic Science, 2014 edition and Basic Science & Technology for Junior Secondary School 1, 2 and 3.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp