fidelitybank

Gwamnatin Tarayya na son rataya min jakar tsaba – Peter Obi

Date:

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour a zaɓen da ya wuce, Peter Obi, ya ce da alama ministan yaɗa labarai, Lai muhammad yana son rataya masa jakar tsaba.

Ya ce ministan yana wannan yunƙuri ne game da wata tattaunawar wayar salula tsakanin Obi da Bishop David Oyedepo, wani babban limamin Kirista na majami’ar Living Faith Church, wadda ta janyo muhawara mai zafi da ce-ce-ku-ce.

Wannan ne karon farko da Peter Obi ya fito ya maida martani game da lamarin, tun bayan kwarmata tattaunawar.

Ya wallafa martanin ne a shafinsa na Tuwita.

Ɓullar sautin dai ya janyo zazzafar muhawara a tsakanin al’ummar Najeriya musamman a shafukan sada zumunta, inda masu adawa da shi ke zargin sa da cewa saɓanin iƙirarin da yake yi a fili, shi ma dai ɗan siyasa ne da ke amfani da ƙabilanci da bambanci addinai don cimma biyan buƙatarsa..

Shi dai Mista Lai Mohammed ya zargi Peter Obi da cin amanar ƙasa, kasancewar a tattaunawar an ji yadda ɗan takarar yake alaƙanta siyasarsa, tamkar wani yaƙi na addini tare da tabbatar wa limamin kirista cewa, (Kiristoci) ba za su yi da na sanin goya masa baya ba.

Har ma Obi yana roƙon malamin ya taimaka masa wajen nema masa goyon bayan mabiya addinin kirista da ke kudu maso yammacin Najeriya da kuma shiyyar arewa ta tsakiyar ƙasar.

Peter Obi ya ce abin takaici ne yadda ake ta yunƙurin ɓata masa suna da kuma kasancewar hakan na zuwa ne daga wajen ministan gwamnati.

A cewar Peter Obi, bai taɓa yin wata magana ko kuma ƙarfafa gwiwar a yi wa Najeriya maƙarƙashiya ba sannan ya ce bai taɓa ɗaukar nauyi, ko ma furta wani mummunan abu game da Najeriya ba.

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp