fidelitybank

Gwamnatin Tarayya na neman daukin duniya a kan kare wayoyin teku

Date:

Gwamnatin tarayya na neman sake nazarin dokokin duniya domin kare wayoyin ƙarƙashin teku inda ta ce za ta tattauna da ƙasashe domin hanzarta yunƙurin.

Ministan yaɗa labarai na ƙasar, Bosun Tijjani ne ya bayyana hakan a shafinsa na X.

Tun ranar Alhamis ne, abokanan hulɗar kamfanonin sadarwa da bankuna suka fuskanci matsalar sadarwar intanet saboda katsewar wayoyin ƙarƙashin tekun Atalantik da ke Cote D’Ivoire ta gaɓar tekun yammacin Afirka, lamarin da ya gurgunta harkokin cinikayya ta intanet da sadarwar intanet.

Kamfanin wayoyin ƙarƙashin teku na MainOne ya ce zai ɗauki kusan mako biyu kafin gyara matsalar da ta lalata intanet a Najeriya da Ghana da Cote D’Ivoire da Senegal da wasu ƙasashen yammacin Afirka da na gabashin yankin a kwanaki huɗun da suka gabata.

Kamfanin ya danganta matsalar ga ayyukan masunta da girgizar ƙasa da zaizayewar laka da kuma tangarɗar na’ura.

Ministan a saƙon nasa ya ce matsalar da aka samu za ta taimaka wajen samar da hanyoyin inganta sadarwa a Najeriya.

Ya kuma yaba da shugabancin kamfanin na MainOne da sauran kamfanonin sadarwa a ƙoƙarinsu na taƙaita tasirin katsewar.

Ya kuma bai wa mutanen da ke ci gaba da fuskantar matsala tabbacin cewa hukumar sadarwar Najeriya NCC tana aiki da muhimman masu ruwa da tsaki domin warware matsalar a ƙanƙanin lokaci.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp