fidelitybank

Gwamnatin Taliban ta sanya dokoki ga matan Afghanistan

Date:

Gwamnatin Taliban a kasar Afghanistan ta sanar da cewa, duk macen da ke son yin tafiya, sai ta kasance tare da wani dangi na kusa da ita.

Masu motocin za su baiwa matan da ke sanye da hijabi na Musulunci kawai abin hawa, inji jagorar da ma’aikatar inganta nagarta da rigakafin ta bayyana.

Mai magana da yawun ma’aikatar, Sadeq Akif Muhajir ya bayyana hakan yayin da ya ke magana da kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Lahadi cewa, dole ne ya kasance dangi na kud da kud, “Bai kamata a ba matan da ke tafiya fiye da mil 45 (kilomita 72) ba idan ba su tare da wani dangi na kusa ba”.

Sabon umarnin ya zo ne makonni bayan da ma’aikatar ta bukaci gidajen talabijin na Afganistan da su daina nuna wasan kwaikwayo na tallan sabulu da ke nuna mata ‘yan wasan kwaikwayo.

Ma’aikatar ta kuma yi kira ga mata ‘yan jarida na TV da su sanya hijabi yayin gabatar da su.

Ministan ya kara da cewa, za a kuma bukaci mata masu neman abin hawa su sanya hijabi. Umarnin na ma’aikatar ya kuma bukaci mutane da su daina kida a cikin motocinsu.

A halin da a ke ciki, ba a fayyace fassarar da Taliban ta yi wa hijabi ba, saboda yawancin matan Afghanistan sun riga sun sanya hijabi.

Tun bayan da kungiyar ta Taliban ta karbi mulki a watan Agusta, ta kakaba takunkumi iri-iri kan mata da ‘yan mata, duk da cewa sun yi alkawarin kafa wata doka mai sassauci idan a ka kwatanta da mulkinsu na farko a shekarun 1990.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuÉ—in gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuÉ—in gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...
X whatsapp