fidelitybank

Gwamnatin Taliban ta sanya dokoki ga matan Afghanistan

Date:

Gwamnatin Taliban a kasar Afghanistan ta sanar da cewa, duk macen da ke son yin tafiya, sai ta kasance tare da wani dangi na kusa da ita.

Masu motocin za su baiwa matan da ke sanye da hijabi na Musulunci kawai abin hawa, inji jagorar da ma’aikatar inganta nagarta da rigakafin ta bayyana.

Mai magana da yawun ma’aikatar, Sadeq Akif Muhajir ya bayyana hakan yayin da ya ke magana da kamfanin dillancin labarai na AFP a ranar Lahadi cewa, dole ne ya kasance dangi na kud da kud, “Bai kamata a ba matan da ke tafiya fiye da mil 45 (kilomita 72) ba idan ba su tare da wani dangi na kusa ba”.

Sabon umarnin ya zo ne makonni bayan da ma’aikatar ta bukaci gidajen talabijin na Afganistan da su daina nuna wasan kwaikwayo na tallan sabulu da ke nuna mata ‘yan wasan kwaikwayo.

Ma’aikatar ta kuma yi kira ga mata ‘yan jarida na TV da su sanya hijabi yayin gabatar da su.

Ministan ya kara da cewa, za a kuma bukaci mata masu neman abin hawa su sanya hijabi. Umarnin na ma’aikatar ya kuma bukaci mutane da su daina kida a cikin motocinsu.

A halin da a ke ciki, ba a fayyace fassarar da Taliban ta yi wa hijabi ba, saboda yawancin matan Afghanistan sun riga sun sanya hijabi.

Tun bayan da kungiyar ta Taliban ta karbi mulki a watan Agusta, ta kakaba takunkumi iri-iri kan mata da ‘yan mata, duk da cewa sun yi alkawarin kafa wata doka mai sassauci idan a ka kwatanta da mulkinsu na farko a shekarun 1990.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuÉ—in...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp