Ƙungiyar Taliban ta ce, ta aiwatar da hukuncin kisa karon farko tun bayan da ta ƙwace mulki a Afghanistan a shekarar da ta gabata.
A cikin wata sanarwa, Taliban ta ce an kashe wani mutum mai suna Dajmir, saboda ya amsa laifin yin kisa.
Kakakin ƙungiyar ya ce an aiwatar da hukuncin ne a wani filin ƙwallon ƙafa da ke Lardin Farah a Kudu Maso Yammacin ƙasar.
Wasu manyan jami’an gwamnati sun halarci wajen ciki har da ministan harkokin cikin gida da ministan harkokin waje.