Sabbin hukumomin mulki a Syria sun ce suna shirin rufe gidajen yarin hamɓararren shugaban ƙasar Bashar al-Assad tare da rusa rundunar jami’an tsaronsa.
Dubbban mutane ne ake tunanin gwamnatin Assad ke tsare da su a gidajen yarin na Syria, ciki har da katafaren ginin nan na Sednaya, inda ake yawan samun rahotannin azabtarwa.
Tun bayan da ‘yantawayen ƙasar suka kifar da gwamnatin Assad suka yi ta buɗe gidajen yarin domin sakin fursunoni.