Gwamnatin jihar Sokoto, ta sassauta dokar hana fita ta sa’o’i 24 da ta kafa a jihar, sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke kan kama waɗanda ake zargi sun kashe ɗalibar da ake zargi ta yi ɓatanci ga Manzon Allah S.A.W.
Daruruwan musulmi ne suka fito kan titi suna neman a sako wadanda ake zargi da hannu a kisan wata daliba da ake zargi da yin batanci ga addinin Musulunci.
Amma zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tashin hankali tare da kona tayoyi a kan tituna, da wawashe shaguna da kuma toshe manyan tituna kafin jami’an tsaro suka harba hayaki mai sa hawaye, domin tarwatsa masu zanga-zangar. Lamarin da ya sa gwamnan jihar Aminu Waziri Tambuwal ya kafa dokar hana fita.
A wata sanarwa daga kwamishinan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na jihar Sokoto, Isah Bajini Galadanci ya fitar, ya ce, bayan nazarin yanayin tsaro, an sassauta dokar ta bacin, inda ta koma daga magariba zuwa wayewar gari.
A cewar gwamnati, an yi hakan ne domin ba mutane damar gudanar da harakokinsu na yau da kullum. In ji BBC.
Gwamnatin jihar, duk da haka, ta yi kira ga al’ummar Sokoto da su kasance masu zaman lafiya, tana mai cewa ”ba za a amince da duk wanda ya keta doka da oda ba”’.