fidelitybank

Gwamnatin Sokoto ta sassauta dokar hana fita

Date:

Gwamnatin jihar Sokoto, ta sassauta dokar hana fita ta sa’o’i 24 da ta kafa a jihar, sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke kan kama waɗanda ake zargi sun kashe ɗalibar da ake zargi ta yi ɓatanci ga Manzon Allah S.A.W.

Daruruwan musulmi ne suka fito kan titi suna neman a sako wadanda ake zargi da hannu a kisan wata daliba da ake zargi da yin batanci ga addinin Musulunci.

Amma zanga-zangar ta rikiɗe zuwa tashin hankali tare da kona tayoyi a kan tituna, da wawashe shaguna da kuma toshe manyan tituna kafin jami’an tsaro suka harba hayaki mai sa hawaye, domin tarwatsa masu zanga-zangar. Lamarin da ya sa gwamnan jihar Aminu Waziri Tambuwal ya kafa dokar hana fita.

A wata sanarwa daga kwamishinan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na jihar Sokoto, Isah Bajini Galadanci ya fitar, ya ce, bayan nazarin yanayin tsaro, an sassauta dokar ta bacin, inda ta koma daga magariba zuwa wayewar gari.

A cewar gwamnati, an yi hakan ne domin ba mutane damar gudanar da harakokinsu na yau da kullum. In ji BBC.

Gwamnatin jihar, duk da haka, ta yi kira ga al’ummar Sokoto da su kasance masu zaman lafiya, tana mai cewa ”ba za a amince da duk wanda ya keta doka da oda ba”’.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...

Ni da Wike tif da taya ne – Fubara

Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya ce, babu...

Za a yi jana’izar Dantata a ranar Litinin

Babban sakataren marigayi Alhaji Aminu Dantata, Mustapha Abdullahi Junaid,...

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...
X whatsapp