fidelitybank

Gwamnatin Sokoto ta kafa kwamitin siyar da Shinkafa mai sauƙi

Date:

Gwamnatin jihar Sokoto ta sanar da yunƙurinta na fara sayar da shinkafa da sauran kayayyakin abinci, inda za ta sayar da su da ragowar kashi 55 na farashin kayayyakin abincin, wanda da ta sayo na naira biliyan 14.

Gwamna Ahmed Aliyu ne ya sanar da hakan a lokacin da yake ƙaddamar da kwamitin bibiya da sa ido a kan sayar da kayan abinci a yau Litinin, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Gwamnan ya ce sun ɗauki wannan matakin ne domin rage wa mutane raɗaɗdin da suke ciki na tsananin rayuwa tun bayan cire tallafin man fetur, inda ya ce abincin zai kai dukkan mazaɓun jihar guda 244.

“Ku guji sanya bambancin siyasa ko addini wajen sayar da kayayyakin abincin. Wannan abinci ne na dukkan ƴan jihar Sokoto.” in ji shi.

Ya kuma ƙara da cewa gwamnatinsa za ta cigaba da aiwatar da tallafi irin haka har zuwa lokacin da tattalin arzikin ƙasar zai bunƙasa.

A ƙarshe ya yi kira ga masu hannu da shuni a jihar da kamfanoni, da su taimaka wajen rage wa mutane halin raɗaɗin da mutane suke ciki.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp