Makonni uku a gudanar da zaben gwamna a jihar Osun, gwamnatin jihar ta ayyana ranar Juma’a 24 ga watan Yuni a matsayin ranar da babu aiki, domin baiwa ma’aikatan da har yanzu basu karbi katin zabe na dindindin ba.
A cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar a ranar Alhamis, ta ce, an samu ci gaban ne domin baiwa dukkan ma’aikatan gwamnati damar karbar katin zabe na PVC, domin samun damar gudanar da aikinsu a zaben gwamna da za a gudanar a ranar 16 ga watan Yuli.
Hakan ya fito ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Prince Wole Oyebamiji.
Sanarwar ta kara da cewa: “Gwamnatin jihar Osun ta amince da muhimmancin ma’aikata a tsarin dimokuradiyya, kuma tana sane da cewa, hanya daya tilo da ma’aikata za su iya cimma burinsu na samar da gwamnatin da ta dace da ma’aikata ita ce ta kuri’unsu.