Gwamnati jihar Neja ta saka dokar ta baci na tsawon sa’a 24 a wasu kananan hukumomin Shiroro da Rafi.
Gwamnatin ta sanya dokar ta bacin ne, sakamakakon yawan hare-haren da ‘yan bindiga su ke kaiwa yankunan.
Gwamnatin Neja ta samu rahotanin sirri kan cewa, ‘yan bindigan masu dimbin yawa za su kai farmaki cikin jihar, hakan zai bada damar zakulo ‘yan ta’addan da suke shirin kai har yankin, a cewar kwamishanan kula da al’amuran masarautu da tsaron cikin gida. A cewar jaridar The Nation.
Am sami labarin yadda aka umarci mazauna Rafi da Shiroro da su zauna a gidajen su daga karfe 5:00 na yammacin Asabar har sai baba ta gani. An hana jama’a mazaunan kauyukan Kuta, Gwada da Zumba fita, inda aka hada su da sojoji masu tarin yawa da ke tsaron su.