fidelitybank

Gwamnatin Neja ta gayyaci shugab da malamin da suka haɗa muhawara ɗalibi ya caccaki Tinubu

Date:

Gwamnatin jihar Neja ta gayyaci malami da kuma shugaban makarantar firamare ta Kassim da ke karamar hukumar Agaie a kan wani faifan bidiyo da ya nuna wani dalibi yana amfani da abin da aka bayyana da kalaman batanci a yayin wata muhawara.

A cikin faifan bidiyon, dalibin mai suna Abdulkabir Abdulkadir, ya nuna rashin amincewarsa da kudirin neman kada kuri’a a Najeriya.

Ya bayyana damuwarsa kan yadda siyasar kasar nan ke ciki, ya kuma soki shugaba Bola Tinubu, inda ya bayyana cewa shugabancinsa ya jawo wa al’umma wahala.

Da take mayar da martani kan faifan bidiyon, Kwamishiniyar ilmin asali da sakandare a jihar Neja, Hadiza Mohammed, ta yi Allah-wadai da zabar kalmomin da dalibar ke amfani da su.

Ta bayyana abin da ke cikin bidiyon a matsayin “mai tayar da hankali” kuma ta ce da alama an koyawa dalibin yin amfani da kalamai na tashin hankali da rashin kunya wajen gabatar da shi.

Ma’aikatar ta gayyaci malamin ajin da shugaban makarantar don yin taka-tsantsan, inda ta bayyana bukatar dalibai su guji yin amfani da kalaman tashin hankali, musamman da yake yaron yaro ne.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp