Gwamnatin jihar Neja ta ce, ba ta da masaniyar cewa, mutane na zaune a unguwar Kurebe da ke karamar hukumar Shiroro a jihar,, inda aka ce harin da sojojin saman Najeriya suka kai a sama ya kashe yara shida tare da lalata gidaje.
Gwamnatin jihar ta ce an yi zaton wurin ba kowa ne, saboda ci gaba da ayyukan ‘yan bindiga da aka yi a yankin na tsawon wani lokaci.
Kwamishinan kananan hukumomi, masarautu da tsaro na cikin gida, Emmanuel Umar, wanda ya bayyana haka a ranar Alhamis a Minna, babban birnin jihar, ya tabbatar da cewa ana ci gaba da kai sama da fadi da sojoji da sauran hukumomin tsaro a jihar.
“A iya sanin gwamnatin jihar, babu wani farar hula da ke zaune a wadannan yankuna na wani dan lokaci, sakamakon kutsawa da ayyukan ‘yan ta’adda da ya tilastawa mazauna yankin neman mafaka a matsayin ‘yan gudun hijira a wasu sassan jihar,” inji shi. .
Umar ya ce gwamnatin jihar ta yi marhabin da yadda ake ci gaba da zafafa ayyukan soji a jihohin da ke makwabtaka da jihar da kuma wasu kananan hukumomin jihar da suka hada da Shiroro, Munya da sauransu da nufin kawar da ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda a cikin muhalli.