Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Maitama Tuggar, ya jogoranci wata tawagar gwamnati domin kai ziyarar aiki zuwa Jamhuriyar Nijar.
Wannan shi ne karon farko da ministan harkokin wajen Najeriya ke ziyara a Jamhuriyar Nijar tun bayan juyin mulkin da ya hamɓarar da gwamnatin Mohammed Bazoum a shekarar 2023.
An fara takun saƙar diflomasiyya tsakanin ƙasashen biyu bayan dangantaka ta yi tsami tsakanin gwamnatin mulkin sojin Nijar da kuma ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afrika (ECOWAS) wanda shugaban Najeriya ke jagoranta.