Gwamnatin ƙasar Mali karkashin jagorancin sojin kasar ta bayar da umarnin cire tashar talabijin na France 2 daga yaɗa shirye-shiryenta na tsawon watanni hudu bayan da tashar ta watsa wani labarin da hukumomin kasar suka dauka a matsayin “neman uzuri ga masu aikata ta’addanci”.
Labarin, wanda ya shafi yanayin tsaro a Mali, an watsa shi ne a ranar 20 ga watan Janairu.
Hukumar Kula da Sadarwa ta Mali (HAC) ta zargi gidan tashar da “ingiza aikata ta’addanci” ta hanyar kwatanta “karfin kungiyoyin ta’addanci” da na sojojin ƙasar.
HAC ta kuma zargi tashar da gaza jin ta-bakin mahukuntan Mali kafin watsa labarin da kuma “mummunan keta dokar aikin jarida.
Wannan dai ba shi ne mataki na farko da ƙasar Mali ta dauka a kan kafafen yada labaran Faransa ba.
A shekarar 2022, gwamnatin mulkin soja ta dakatar da France 24 da Radio France Internationale.
Dangantaka dai tsakanin Mali da tsohuwar ƙasar da ta yi mata mulkin mallaka, Faransa ta tabarbare tun bayan da shugaban mulkin sojan kasar Kanar Assimi Goita ya kwace mulki a shekara ta 2021.