Gwamnatin jihar Legas ta dauki nauyin gurfanar da dan sandan da ya harbe Bolanle Raheem har lahira.
An kashe lauyan ce bayan da ASP Drambi Vandi ya bude wuta a ranar Kirsimeti bayan ya caccakar Bolanle da mijinta.
Vandi da tawagarsa, yanzu haka suna tsare, sun kasance a ofishin ‘yan sanda na Ajiwe da ke Ajah.
Kungiyar lauyoyin Najeriya (NBA) ta yi kira da a yi cikakken bayani kan abin da ya faru a ranar Lahadi.
A ranar Talata, Gwamna Babajide Sanwo-Olu ya bayyana matsayinsa na yin adalci ga iyali.
Sanwo-Olu ya aika da tawagar manyan jami’ai domin ta’aziyyar ‘yan uwa a gidansu da ke Ajah.
Tawagar ta samu jagorancin babban lauya kuma kwamishinan shari’a Moyo Onigbanjo, SAN, wanda ya bayyana cewa jihar za ta gurfanar da shi gaban kotu.
“Muna da izinin Maigirma Gwamna mu gaya muku cewa za a yi adalci a wannan lamarin. Za a gurfanar da lamarin gaban kotu da zarar ‘yan sanda sun aiko mana da fayil din karar.
“Zan jagoranci masu gabatar da kara don nuna muhimmancin gwamnati game da wannan batu,” in ji Onigbanjo.
Mijin marigayi Bolanle, Gbenga Raheem ya godewa Sanwo-Olu kan yadda ya tausaya masa.
Sauran da ke cikin tawagar sun hada da shugaban ma’aikata Muri Okunola, kwamishinan mata da yaki da talauci, Bolaji Dada, kwamishinan yada labarai, Gbenga Omotoso, da kuma mai ba da shawara na musamman Tubosun Alake.