Ƴan Najeriya na mayar da martani tare da nuna kaɗuwarsu kan sace tare da kashe wata matashiya da aka yi a jihar Legas.
A na tuhumar daya daga cikin direbobin motar wadda mallakar gwamnati ce, wadda aka fi sani da sunan BRT (Bus Rapid Transit), kuma an kama shi, ana tuhumars ada aikata wannan mummunan laifin.
Matar mai shekara 22 ta bace ne tun karshen watan Fabrairu, bayan da ta shiga motar ta BRT mai farin jini.
Labarin abin da ya faru ga matar ya tayar da hankulan jama’a har ta kai ga an fara wani gangami a shafukan sada zumunta, inda ake neman adalci ga matar: Justice for Bamise a Twitter.
Gwamnatin jihar Legas ta kuma yi alkawarin daukar matakin shari’a kan duk wanda aka samu ya na da hannu kan sacewa da hallaka matar.