fidelitybank

Gwamnatin Legas ta rufe kasuwannin jihar 13

Date:

Gwamnatin jihar Legas ta sanar da rufe wasu kasuwannin jihar 13, sakamakon saɓa doka kan zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan Muhalli da albarkatun ruwan sha na jihar, Tokunbo Wahab ya wallafa a shafinsa na X, ranar Juma’a ya ce matakin ya zama wajibi domin tsaftace muhalli da inganta lafiyar al’ummar jihar.

Kwamishinan ya ce an ɗauki matakin ne bisa la’akari da dokokin kare muhalli na jihar da aka yi wa gyaran fuska a 2017, da nufin tabbatar da zuba shara a wuraren da suka dace da bin dokokin gwamnati.

Mafi yawan kasuwannin da aka rufe na yankunan Ketu da Mile 12 – waɗanda aka rufe jiya da daddare saboda ci gaba da saɓa doka, ciki har da zuba shara a kan hanyoyi da manyan titunan jihar.

Ga jerin kasuwannin da gwamnatin ta rufe kamar yadda kwamishinan ya wallafa a shafin nasa

  • Kasuwar Erukan da ke Mile 12
  • Kasuwar Oja Oba da ke Ketu
  • Kasuwar Owoseni Tundas
  • Kasuwar Oba Ogunjobi da ke Mile 12
  • Kasuwar Shops Owners (BRT Terminal) da ke Mile 12
  • Kasuwar tashar motoci ta Mile 12
  • Kasuwar Ketu Terminal (6 plazas)
  • Kasuwar Ifesowapo da ke Mile 12
  • Rukunin shagunan Demurin St Plaza, Ketu
  • Kasuwar The Occupant, da ke kan titin Demurin, Ketu
  • Kasuwar Ifelodun da ke Ketu
  • Kasuwar tashar Ibadan (da ke tsakanin kasuwar Babajide Sanwo-Olu da ta kayan gwari ta Ikosi)
  • Kasuwar Tipper Garage da ke Ketu

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp