fidelitybank

Gwamnatin Legas ta rufe kasuwannin jihar 13

Date:

Gwamnatin jihar Legas ta sanar da rufe wasu kasuwannin jihar 13, sakamakon saɓa doka kan zubar da shara ba bisa ƙa’ida ba.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan Muhalli da albarkatun ruwan sha na jihar, Tokunbo Wahab ya wallafa a shafinsa na X, ranar Juma’a ya ce matakin ya zama wajibi domin tsaftace muhalli da inganta lafiyar al’ummar jihar.

Kwamishinan ya ce an ɗauki matakin ne bisa la’akari da dokokin kare muhalli na jihar da aka yi wa gyaran fuska a 2017, da nufin tabbatar da zuba shara a wuraren da suka dace da bin dokokin gwamnati.

Mafi yawan kasuwannin da aka rufe na yankunan Ketu da Mile 12 – waɗanda aka rufe jiya da daddare saboda ci gaba da saɓa doka, ciki har da zuba shara a kan hanyoyi da manyan titunan jihar.

Ga jerin kasuwannin da gwamnatin ta rufe kamar yadda kwamishinan ya wallafa a shafin nasa

  • Kasuwar Erukan da ke Mile 12
  • Kasuwar Oja Oba da ke Ketu
  • Kasuwar Owoseni Tundas
  • Kasuwar Oba Ogunjobi da ke Mile 12
  • Kasuwar Shops Owners (BRT Terminal) da ke Mile 12
  • Kasuwar tashar motoci ta Mile 12
  • Kasuwar Ketu Terminal (6 plazas)
  • Kasuwar Ifesowapo da ke Mile 12
  • Rukunin shagunan Demurin St Plaza, Ketu
  • Kasuwar The Occupant, da ke kan titin Demurin, Ketu
  • Kasuwar Ifelodun da ke Ketu
  • Kasuwar tashar Ibadan (da ke tsakanin kasuwar Babajide Sanwo-Olu da ta kayan gwari ta Ikosi)
  • Kasuwar Tipper Garage da ke Ketu

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp