fidelitybank

Gwamnatin Legas ta kaddamar da rigakafin Diphtheria bayan an samu Dalibi ya mutu

Date:

Jam’ian kiwon lafiya a jihar Legas sun ƙaddamar da shirin riga-kafi na gaggawa bayan samun ɓarkewar cutar Diphtheria da ya yi sanadiyyar mutuwar wani ɗalibi mai shekara 12 a wata makarantar sakandare.

Aƙalla mutane 34 suka yi mu’amala da shi kuma ana sanya musu ido, yayin da ɗalibai 14 daga makarantar kwanan mai suna King’s College suka nuna alamu kuma aka tabbatar da cewa 12 daga cikinsu na da cutar, inda tuni aka fara ba su magani.

A cewar ma’aikatar lafiya ta jihar Legas, yaron ya fara nuna alamu ne na ciwon maƙoshi da kuma zazzaɓi a cibiyar lafiya ta makarantar a ranar 22 ga watan Fabrairu, inda kuma ya rasu a ranar 6 ga watan Maris.

A yanzu haka an fara gangamin yi wa mutane riga-kafi musamman yara da jam’ian kula da lafiya na makarantar, wanda hukumomi ke ganin za a faɗaɗa shi zuwa jihar baki-ɗaya.

Wata takardar gargaɗi kan lafiya ta buƙaci mazauna jihar su mayar da hankali kan tsafta da kuma guje wa shiga cunkoson mutane kuma su garzaya asibiti da zarar sun fara jin alamu irin na cutar diphtheria.

Kwamishinan lafiya na jihar Farfesa Akin Abayomi ya tabbatar wa da alumma cewa babu buƙatar su tayar da hankalinsu ganin cewa ana iya ƙoƙari wajen daƙile ɓarkewar cutar, kuma za a ci gaba da ɗaukar matakai domin kare su daga kamuwa da ita.

A shekarar 2023 ne aka samu ɓarkewar cutar diphtheria mafi girma a Najeriya inda ta yi sanadiyyar mutuwar mutane fiye da 600 akasari yara, kuma cutar ta shafi jihohi 19 cikin 36 da ke ƙasar.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp