fidelitybank

Gwamnatin Legas ta fara bincike a kan korar daliba saboda Obi

Date:

Gwamnatin jihar Lagos ta fara gudanar da bincike kan zargin da ake yi cewa, wani shugaban makaranta ya kori ɗaliba saboda ta naɗe bangon littafinta da hoton ɗan takarar shugabn ƙasa na jam’iyyar Labour Peter Obi.

A wata sanarwa da mataimakin darektan hulɗa da jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Ganiu Lawal, ya fitar ya ce, gwamnati ta gayyaci shugaban makarantar inda za ta nemi ya yi bayani kan lamarin.

Karanta Wannan: Ina da kwarin gwiwa kotu za ta kwato min kujera ta a wajen Tinubu – Obi

Mahaifiyar ɗalibar ta sanya labarin abin da ta ce ya faru da ƴar tata mai shekara 10 ne a shafin sada zumunta da muhawara, wanda hakan ya sa labarin ya bazu ake ta ce-ce-ku-ce a kai, har gwamnati ta ɗauki matakin binciken.

Kwamishinar ilimi ta jihar ta Lagos Mrs Folashade Adefisayo a sanarwar ta bai wa jama’a tabbacin cewa za a ɗauki matakin da ya dace kan lamarin bisa abin da doka ta tanada, domin a cewarta dalilin korar yarinyar ba abin da za a lamunta ba ne, idan har ya tabbata hakan.

A ranar Talata ne rahotanni labarin ya bayyana cewa shugaban ƙaramar sakandire ta Odomola, da ke Epe a Lagos ya kori ɗaliba Marvellous Barinaadaa zuwa gida saboda ta nade bangon littafinta da hoton Peter Obim, wato ɗan takarar jam’iyyar Labour, da ya zo na uku a sakamakon zaɓen shugaban Najeriyar da hukuma ta bayyana.

vanguardnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...
X whatsapp