Gwamnatin jihar Lagos ta fara gudanar da bincike kan zargin da ake yi cewa, wani shugaban makaranta ya kori ɗaliba saboda ta naɗe bangon littafinta da hoton ɗan takarar shugabn ƙasa na jam’iyyar Labour Peter Obi.
A wata sanarwa da mataimakin darektan hulɗa da jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Ganiu Lawal, ya fitar ya ce, gwamnati ta gayyaci shugaban makarantar inda za ta nemi ya yi bayani kan lamarin.
Karanta Wannan: Ina da kwarin gwiwa kotu za ta kwato min kujera ta a wajen Tinubu – Obi
Mahaifiyar ɗalibar ta sanya labarin abin da ta ce ya faru da ƴar tata mai shekara 10 ne a shafin sada zumunta da muhawara, wanda hakan ya sa labarin ya bazu ake ta ce-ce-ku-ce a kai, har gwamnati ta ɗauki matakin binciken.
Kwamishinar ilimi ta jihar ta Lagos Mrs Folashade Adefisayo a sanarwar ta bai wa jama’a tabbacin cewa za a ɗauki matakin da ya dace kan lamarin bisa abin da doka ta tanada, domin a cewarta dalilin korar yarinyar ba abin da za a lamunta ba ne, idan har ya tabbata hakan.
A ranar Talata ne rahotanni labarin ya bayyana cewa shugaban ƙaramar sakandire ta Odomola, da ke Epe a Lagos ya kori ɗaliba Marvellous Barinaadaa zuwa gida saboda ta nade bangon littafinta da hoton Peter Obim, wato ɗan takarar jam’iyyar Labour, da ya zo na uku a sakamakon zaɓen shugaban Najeriyar da hukuma ta bayyana.