fidelitybank

Gwamnatin Kogi ta rufe kamfanin sadarwa na Glo da Airtel

Date:

Hukumar tattara kudaden shiga ta jihar Kogi (KGIRS), ta ce, ta rufe cibiyoyin sadarwa na Globacom da Airtel, saboda gaza biyan harajin sama da Naira miliyan 360.

Saidu Okino, darakta mai kula da harkokin shari’a da tabbatar da doka na KGSIRS, ya jagoranci tawagar jami’an tsaro wajen rufe wuraren da ke Dutsen Patti a Lokoja da kuma fadin jihar.

Mista Okino, wanda ya samu wakilcin shugaban sashen tabbatar da tsaro na ma’aikatar kudaden shiga, Abubakar Obori, ya koka da yadda kamfanonin sadarwar biyu suka ki biyan harajin da ya rataya a wuyan jihar.

Ya ce, “Abin takaici ne yadda kamfanonin biyu suka ci gaba da kaucewa biyan bukatunsu ga jihar, kuma sun tara bashin Naira 360,035,000.00,” in ji Mista Okino.

“A bayanin mu, Globacom Nigeria Ltd., jihar Kogi, harajin da ba a biya ba, ya kai Naira miliyan 300,000,000, yayin da na Airtel ya kai Naira miliyan 60,035,000. Waɗannan alawus-alawus na kamfanonin biyu da suka yi kasala wajen biya mun rufe duka kamfanoni”.

Mista Okino ya kara da bayyana cewa, an rubuta “wasiku da dama” ga kamfanonin biyu, domin su kwantar da hankulan su don biyan harajin da suke bin gwamnatin Kogi, “amma ba su taba nuna wata alama ba.

Ya bayyana cewa rufe shafuka da kadarori na kamfanonin sadarwa ya kasance bisa umarnin kotu.

Mista Okino ya gargadi sauran kamfanonin da ke aiki a jihar da su rinka biyan kudaden harajin da ake bin su a kodayaushe, domin kaucewa fushin doka.

legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp