fidelitybank

Gwamnatin Kebbi ta rufe kwalejin kiwon lafiya a Jega bayan boren ɗalibai

Date:

Gwamnatin jihar Kebbi ta bayar da umarnin rufe kwalejin kiwon lafiya ta Jega, bayan zanga-zanga da ɗalibai suka yi wanda ya rikiɗe zuwa tarzoma.

Kwamishinan ilimi mai zurfi na jihar, Isah Abubakar Tunga ne ya sanar da haka ga manema labarai, inda ya ce ɗaukar matakin ya zama wajibi domin kaucewa yaɗuwar rikicin.

Ɗaliban sun ce sun shiga zanga-zangar ne domin nuna fushinsu kan rashin yi wa wasu kwasa-kwasai rajista, rashin kyawun wurin zama da kuma rashin shugabanci na gari.

An nuna wasu ɗalibai sun far wa gidan shugaban kwalejin, inda suka cinna wa gidansa wuta da kuma lalata motarsa.

Tunga ya tabbatar da cewa za a kafa wani kwamiti domin gudanar da bincike kan lamarin.

Ya kuma ce za a hukunta duk wanda aka samu da hannu a lamarin.

Yanzu dai kwalejin zai ci gaba da zama a rufe har na tsawon makonni uku, a cewar gwamnatin jihar.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp