fidelitybank

Gwamnatin Katsina za ta raba shinkafa mutane 33,000

Date:

Gwamnatin jihar Katsina ta c,e za ta raba shinkafa ga tsofaffi da masu bukata ta musamman da ma gajiyayyu kimanin 33,000 a fain jihar.

Cikin wani sako da gwamnan jihar Dikko Umaru Radda ya wallafa a shafinsa na Facebook, ya ce a kokaruin da gwamnatinsa ke yi magance matsin rayuwa da tsadar hatsi, gwamnatin jihar za ta raba hatsi a kan farashi mai rahusa da za a sayar kan kudi naira 20,000 kowane buhu, don agaza wa masu karamin karfi a jihar.

”Hatsin da za a sayar kan wannan farashin su ne masara, gero, da dawa”, in ji sanarwar.

Gwamnan ya ce kowane dan jihar na da damar sayen mudu (tiya) goma na hatsin kuma kowace tiya daya, za a sayar da ita kan kudi naira 500, idan aka kwatanta da farashin kasuwa a yanzu da ake sayarwa kusan naira 1,500, kamar yadda sanarwar ta yi bayani.

Gwamna Radda ya kuma ce gwamnati za ta rika daukar nauyin dafa abinci a kowace rana cikin watan azumin Ramadan a fadin duka mazabun jihar 361 domin rage wahalhalun da tsadar rayuwa da al’ummar kasa ke fuskanta.

”Bugu da kari, za a yi kokarin tallafa wa manoma da karfafa aikin noma domin rage dogaro da hanyoyin samar da abinci daga waje”, in ji gwamnan.

Tun bayan cire tallafin man fetur a shekarar da ta gabata dai shugaban kasar Bola Tinubu ya bukaci gwamnonin jihohin kasar su rika bullo da sabbin hanyoyin tallafa wa talakawan kasar don rage musu radadi.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp