fidelitybank

Gwamnatin Kano za ta yi wa yara miliyan 3.6 rigakafin shan inna

Date:

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano, ta kammala shirin yi wa yara miliyan 3.6 allurar rigakafin cutar shan inna ta novel type 2 ta baki (nOPV2) a wani mataki na mayar da martani ga barkewar cutar poliovirus mai saurin yaduwa a jihar.

A cikin lokaci guda ne dai, ma’aikatar ta kaddamar da shirin makon kiwon lafiyar jarirai da mata masu juna biyu (MNCHW), domin rage yawan mace-macen da ake samu, inda za a kashe sama da Naira biliyan 2.5 wajen gudanar da ayyukan biyu.

Da ya ke jawabi ga manema labarai a ranar Juma’a, kwamishinan lafiya na jihar, Dr. Aminu Ibrahim Tsanyawa ya bayyana cewa, hadaddiyar kamfen na OBRI da MNCHW za su gudana ne a lokaci guda daga ranakun 9 ga Alhamis 13 ga watan Janairu 2022.

Dr. Tsanyawa ya yi bayanin cewa, ingantattun allurar rigakafin cutar shan inna ta zama dole, domin samun nasarar kawar da cutar shan inna ta duniya (GPEI).

Kwamishinan ya yi nadamar cewa shekaru uku bayan da Najeriya ta samu kasar da ba ta da cutar shan inna, an gano bullar cutar shan inna mai nau’in 2 (cVDPV2) a jihohi 13 na tarayyar kasar ciki har da Kano tare da samun mutum 106 da suka kamu da cutar a fadin kananan hukumomin 25.

Dr. Tsanyawa ya kuma yi kira ga iyaye tare da mata masu juna biyu da su yi amfani da wannan damar na samar da lafiyar ƴaƴan su.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp