fidelitybank

Gwamnatin Kano za ta yi wa yara miliyan 3.6 rigakafin shan inna

Date:

Ma’aikatar lafiya ta jihar Kano, ta kammala shirin yi wa yara miliyan 3.6 allurar rigakafin cutar shan inna ta novel type 2 ta baki (nOPV2) a wani mataki na mayar da martani ga barkewar cutar poliovirus mai saurin yaduwa a jihar.

A cikin lokaci guda ne dai, ma’aikatar ta kaddamar da shirin makon kiwon lafiyar jarirai da mata masu juna biyu (MNCHW), domin rage yawan mace-macen da ake samu, inda za a kashe sama da Naira biliyan 2.5 wajen gudanar da ayyukan biyu.

Da ya ke jawabi ga manema labarai a ranar Juma’a, kwamishinan lafiya na jihar, Dr. Aminu Ibrahim Tsanyawa ya bayyana cewa, hadaddiyar kamfen na OBRI da MNCHW za su gudana ne a lokaci guda daga ranakun 9 ga Alhamis 13 ga watan Janairu 2022.

Dr. Tsanyawa ya yi bayanin cewa, ingantattun allurar rigakafin cutar shan inna ta zama dole, domin samun nasarar kawar da cutar shan inna ta duniya (GPEI).

Kwamishinan ya yi nadamar cewa shekaru uku bayan da Najeriya ta samu kasar da ba ta da cutar shan inna, an gano bullar cutar shan inna mai nau’in 2 (cVDPV2) a jihohi 13 na tarayyar kasar ciki har da Kano tare da samun mutum 106 da suka kamu da cutar a fadin kananan hukumomin 25.

Dr. Tsanyawa ya kuma yi kira ga iyaye tare da mata masu juna biyu da su yi amfani da wannan damar na samar da lafiyar ƴaƴan su.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp