Gwamnatin jihar Kano za ta sayo jiragen ruwa guda 3 tare da rigunan da ake sawa a cikin ruwa na hana nutsewa, sakamakon sakamakon hadarin kwale-kwale da ya yi sanadin mutuwar mutane 29 a karamar hukumar Bagwai ta jihar Kano.
Kwamishinan yada labarai na jihar, Muhammad Garba ne ya bayyana hakan a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai, bayan kammala taron majalisar zartarwa, wanda aka gudanar a gidan gwamnati ranar Laraba.
A cewarsa, yayin da aka tabbatar da mutuwar mutane 29, an ceto 7 a raye kuma wasu na jinya a asibiti.
Ya ce”Gwamnatin jihar ta samar da buhun shinkafa guda 120, Gero, Masaraasa, domin rabawa iyalan wadanda abin ya shafa, sannan kuma za a raba musu buhun Sikari 60, za a ba kowane iyalan wadanda abin ya shafa Naira 100,000, wanda ya kai Naira miliyan 10”.
Akalla mutane 29 ne suka mutu bayan wani jirgin ruwa dauke da mutane 49 ya kife a hanyarsu ta zuwa garin Badau domin gudanar da Mauludi a ranar Talata.