Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da kudurin tsare-tsare na nazari da daidaita shekarun yin ritaya ga malaman makarantu tare da kafa wani kwamiti da zai tsara takardu, domin aiwatar da aikin.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai Muhammed Garba ya rabawa manema labarai jiya.
Sanarwar ta bayyana cewa, shirin zai bukaci karin albashi da sauran kudaden alawus-alawus na malaman da ba a tanadarwa a kasafin kudin 2021 ba.
Ta kara da cewa duk da cewa ba a tanadar a cikin kasafin kudin ba, akwai bukatar a kyale sabuwar manufar ta fara aiki daga watan jiya.
Ya kuma ce, kwamitin ya ba da umarnin kafa dalilin da ya dace, domin aiwatar da shirin na bunkasa fannin ilimi a jihar.